Daga: Abdullahi Bashir

Wasu manyan shugabannin jam’iyyar ADC, ciki har da tsohon gwamnan jihar Anambra kuma tsohon dan takarar shugaban Ƙasar a shekarar 2023, Peter Obi, na nazarin yiwuwar ficewa daga jam’iyyar zuwa NDC gabanin babban zaɓen 2027.

Majiyoyi na kusa da Obi sun bayyana cewa wannan mataki na da nasaba da rashin gamsuwa da tsarin tafiyar da jam’iyyar ADC, tare da ƙarin rashin tabbas da ya biyo bayan hukuncin kotun koli.


Hukuncin kotun, wanda aka yanke a ranar Alhamis, duk da cewa wasu na kallonsa a matsayin sassauci na wucin gadi, ya ƙara jefa fargaba a zukatan shugabannin haɗakar siyasar gabanin zaɓen 2027.

Kotun kolin ta soke umarnin baya da ya cire David Mark da Rauf Aregbesola daga mukaman Shugaban Jam’iyya da Sakatare na ƙasa, sai dai hukuncin bai warware rikicin shugabanci gaba ɗaya ba, inda ta mayar da shari’ar zuwa babbar kotun tarayya domin ci gaba da sauraro.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Matar Tsohon Shugaban Ƙasa Shehu Shagari Ta Rasu a Shekaru 89

Daga: Hamza Garba Yakasai Hajiya Sutura Shehu Shagari, matar tsohon shugaban ƙasar Najeriya…

Zulum Ya Ware N12.9bn Don Daukar Nauyin Dalibai 54 ’Yan Borno A Fannin Jiragen Sama Da Injiniyoyi

Daga: Kabir Getso Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da…

Pyramid Radio Za Ta Hada Hannu Da Jami’ar Maryam Abacha Don Inganta Aikin Jarida A Kano

Daga: Yakubu Abubakar Gwagwarwa Gidan Radio tarayya Pyramid FM zai hada hannu…

Kungiyar sakwatawa mazauna jihar Kano ta jaddada kudirinta na tallafawa ‘ya’yan ta domin ganin sun dogara da Kawunansu.

Kungiyar sakwatawa mazauna jihar Kano ta jaddada kudirinta na tallafawa ‘ya’yan ta…