Daga: Bashir Abdullahi
Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Isa Pantami, ya yi watsi da matakin amincewa da Jamilu Gwamna a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Gombe gabanin zaben 2027.

Tun da farko a ranar Lahadi, Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya jagoranci manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar wajen bayyana goyon bayansu ga Gwamna a matsayin wanda zai yi wa APC takarar gwamna.
Sai dai a wata sanarwa da Farfesa Suleiman Mohammed ya sanya wa hannu a madadin kungiyar Pantamiyya Movement, Pantami ya bayyana cewa wannan mataki ya sabawa tanade-tanaden Dokar Zabe ta 2026.

Ya kara da cewa bai dace a tilasta wa jam’iyya dan takara ba tare da bin ka’idojin dimokuradiyya da dokokin zabe ba, yana mai kira ga shugabannin jam’iyyar da su mutunta tsarin da doka ta shimfida domin tabbatar da adalci da gaskiya a harkokin siyasa.