Daga: Shehu Suleiman Sharfadi 

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da bayar da gudummawar Naira miliyan daya kowannensu ga iyalan ‘yan wasa 22 da suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a lokacin da suke dawowa daga gasar wasannin motsa jiki ta kasa.

Gwamnati ta kuma shirya raba kayan abinci da sauran kayan agaji don tallafawa iyalan wadanda abin ya shafa.

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya sanar da hakan a madadin gwamna Abba Kabir Yusuf a wata ziyarar jaje da ya kai asibitin Nasarawa inda aka ajiye gawarwakinsu.

Kwamared Gwarzo ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi ba ga jihar Kano kadai ba har ma da daukacin al’ummar kasar baki daya. Ya yi nuni da cewa wadanda suka rasun matasa ne, ’yan wasa masu kishin kasa, wadanda suka wakilci jihar Kano.

Ya kara da cewa Gwamna Yusuf ya bayar da umarnin a gaggauta sakin tallafin kudi ga iyalai tare da ba da umarnin a samar da duk wani magani da ya dace ga wadanda suka tsira.

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa iyalan wadanda abin ya shafa tare da kula da musibar da ta biyo baya cikin tausayawa da daukar nauyi.

Mataimakin gwamnan ya kuma ziyarci asibitin kwararru na Murtala Mohammed, inda ‘yan wasa bakwai da suka samu raunuka ke karbar kulawa domin jajanta musu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

ANPP Na Bukatar Kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa: Shin APC Zata Fuskanci Barazana ne?

Daga: Yakubu Abubakar Gwagwarwa Masana harkokin siyasa na bayyana cewa jam’iyyar APC…

Zamu Karbi Shawarwarin Hukumar Kiyaye Hadurra Domin Dakile Yawaitar Hadurra A Gadar Dakatsalle

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Gwamnatin jihar Kano ta bukaci hukumar kiyaye hadurra…

Asusun Tsaron Arewa: An Buƙaci Gwamnoni Su Mayar da Hankali Kan Aiwatar da Tsare-tsare

Daga: Abdullahi Bashir An bayyana cewa ƙaddamar da Hukumar Amintattu ta Asusun…

Gwamna Abba Ya Karɓi Baƙuncin Tawagar Gwamnatin Jihar Borno

Daga: Sani Idris Maiwaya Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir…