Daga: Shehu Suleiman Sharfadi

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci hukumar kiyaye hadurra ta kasa ta yi bincike game da musabbabin yawaitar hadurra a gadar dakatsalle shekara da shekaru.

Mataimakin gwamnan jihar Kano a madadin gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ya furta hakan yayin da ayarin hukumar kiyaye hadurra ta kasa karkashin jagorancin malam shehu Muhammad min wanda kwamandan shiyya na hukumar Ahmed umar suka kawo masa ziyarar ta’aziyya.

Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya nuna musu cewar gwamnatin jihar Kano a shirye take da ta karbi dukkan wasu shawarwari da suka shafi hanyoyin da suke jihar Kano da ma kasa baki daya.

Shima anasa bangaren kwamandan shiyya Ahmed Umar ya bayyana cewar sun zo Kano ne domin yin taaziyyar rasuwar yan wasan motsa jiki da hatsarin mota ya rutsa dasu a kan hanyar su ta dawowa gida daga jihar Ogun.

Ya kuma baiwa gwamnatin jihar Kano tabbacin bincikar musabbabin yawaitar hadurra a wannan gadar ta Dakatsalle.

Wakilinmu ya ruwaito cewar, kwamandan shiyyar ya samu rakiyar kwamandojin jihohin Kano, Jigawa, Katsina da Kaduna.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamna Abba Ya Ƙaddamar da Gangamin Rigakafin Masassara a Tofa — Mataki Na Farko a Nahiyar Afirka

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya…

Dalilan Da Yasa Gwamnatin Jihar Kano Ta Jaddada Aniyarta Na Ganin An Biya Diyyar Wadanda Aka Hallaka A Jihar Edo

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi  Wani babban kwamiti wanda gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba…

Hukumar Wayar Da Kan Jama’a Ta Shirya Taron Yanda Za’a Magance Matsalar Kwacen Waya Da Makami A Kano

Daga: Abdulmajid Habib Isah Tukuntawa  Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Kasa reshen…

Jami’an Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababen Hawa ta Jihar Bauchi (BAROTA) sun kai ziyarar koyo ga Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA).

Daga Zakariyya Adam Jigirya Wasu Manyan Jami’an Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababen…