Daga: Mas’ud Mato Garo
Ita dai wannan karramawa ta wakana ne awajen bikin rantsar da sabbin shugabannin kungiyar a babban masallacin kasa dake Abuja ranar Larabar da ta gabata.
Da yake wakiltar gwamna Yusuf a wajen bikin, mataimakinsa Alhaji Murtala Sule Garo, ya karɓi lambar yabon a madadin Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Kungiyar dai tayi la’akari ne da irin goyon bayan da gwamnatin jihar kano ke bai wa mahaddatan Alƙur’ani da ma makarantun Alƙur’ani a faɗin najeriya bakidaya.
Bugu da kari, mataimakin gwamnan Alh Murtala Sule Garo, ya miƙa lambobin yabo ga wasu mutane da sukayi fice wajen bayar da gudunmawar bunƙasa karatu da haddar Alƙur’ani a kasar nan.

Cikin mahalarta taron, akwai tsohon Gwamnan Kano,Malam Ibrahim Shekarau da Shugaban Hukumar kula da Ilimin Almajirai da Yaran da Basa Zuwa Makaranta ta Ƙasa, Dr Muhammad Sani Idris da dai sauran su.