Daga: Mas’ud Mato Garo
Wani ayari na manyan jami’an Gwamnatin Jihar Kano ya kai ziyarar ta’aziyya jihar Sokoto domin nuna alhinin rasuwar Sardaunan Sokoto, Alhaji Abubakar Alhaji.
Mataimakin gwamnan kano Murtala Sule Garo ne ya jagoranci ayarin a madadin Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Sauran wadanda suka da fa masa baya ayayin ta’aziyar sun hadar da Sakataren Gwamnatin Jihar kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, Sarkin Rano, Mai Martaba Muhammad Isa Umar; Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar, Hon. Umar Haruna Doguwa; da Kwamishinar Al’adu da Yawon Buɗe Ido, Hajiya Aisha Lawan Saji, cikin wasu da dama.
Ayarin manyan jami’an na gwamnatin kano, ya isa har zuwa gidan iyalan marigayi Sardaunan Sokoto, inda ya isar da sakon ta’aziyyar Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ga iyalan marigayin.
Kaitsaye kuma ayarin sun ziyarci Fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhd Sa’ad Abubakar na lll, domin isar da sakon ta’aziyyar Gwamna Yusuf gareshi inda sukayi addu’ar Allah ya jikan sa da rahama.