Daga: Abdullahi Bashir

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), ta dakatar dan asusun gwamnatin jihar Osun da ke banki, kwanaki 10 kafin gudanar da zaben gwamna wanda zai gidana a ranar 15 ga Agusta, 2026.

An gano cewa asusun da aka dakatar shi ne ake amfani da shi wajen biyan albashin ma’aikatan gwamnati. Hukumar ta sanya masa matsayin dakatar da duk wata mu’amalar fitar da kuɗi daga asusun (Post No Debit) wanda ke nufin ba za a iya fitar da kudi daga ciki ba.

Wannan mataki ya zo ne ‘yan sa’o’i kadan bayan Gwamna Ademola Adeleke ya bayyana cewa EFCC na shirin dakarar da asusun jihar da na manyan jami’an gwamnati.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da wayar da kai na jihar, Hon. Kolapo Alimi, ya fitar a ranar Laraba, gwamnan ya bayyana wannan yunkuri a matsayin “yunkurin dagula ayyukan gwamnati da gangan domin kawo cikas kafin zabe.”

Gwamna Adeleke ya ce, gwamnatinsa za ta dauki matakin da ya dace na doka don tabbatar da cewa an cire dakatarwar da aka yi domin kada a sha wahalar biyan albashi.

Hukumar EFCC kuma har yanzu ba ta fitar da wata sanarwa ta hukuma ba dangane da lamarin.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Kungiyar Jami’an Tsaro Na Sa Kai Tana Taka Rawar Gani Ba Tare Da An Sanyasu A Tsarin Biyan Albashi Na Kasa

Daga: Ibrahim Sani Gama Kungiyar Jami’an Tsaro na Sa Kai ta Kasa reshen…

Gwamnatin Tarayya Ta Daga Kudin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000 Daga 2027

Daga: Abdullahi Muhammad Abuja — Gwamnatin Tarayya ta amince da karin kudin jarabawar…

Sakon Karrama Jagoran Kwankwasiyya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, A Lokacin Zagayowar Ranar Haihuwarsa

Daga: Zakariyya Adam Jigirya A cikin wani sakon karramawa da aka gabatar…

Zan Yi Amfani Da Shirin GEEP Don Inganta Rayuwar Matasan Nigeria – Hamza Ibrahim Baba

Hamza Ibrahim Baba ya kasance Shugaban hukumar kula da shirin gwamnatin tarayya…