Daga: Abdullahi Muhammad

Abuja — Gwamnatin Tarayya ta amince da karin kudin jarabawar kammala sakandare ta WAEC da NECO, inda ta kayyade sabon kudin zuwa N50,000 ga kowane ɗalibi, wanda zai fara aiki daga shekarar 2027.

Sanarwar ta fito ne daga Daraktan Sashen Ilimin Manyan Makarantun Sakandare na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Adeniji Ibrahim, wanda ya ce matakin ya biyo bayan bukatar da Hukumar Shirya Jarabawar Kasashen Yammacin Afirka (WAEC) ta gabatar na neman a sake duba kudin jarabawar Senior School Certificate Examination (SSCE) da za a gudanar daga shekarar 2027.

A cewar sanarwar, sabon tsarin kudin zai shafi jarabawar WAEC da NECO ga ɗaliban makarantun sakandare a fadin Najeriya, domin samar da daidaito a kudaden da ake karba.

Sai dai sanarwar ba ta yi karin haske kan ko Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da tallafa wa wasu rukunan ɗalibai wajen biyan kudin jarabawar ba, ko kuma dalilan da suka sa aka amince da karin kudin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Kano Na Cigaba Da Yiwa Ilimi Gata Don Kyautata Rayuwar Al’umma – Hon. Rabiu

Daga: Kabir Getso Gwamnatin Kano na ciga ba da yiwa ilimi gata…

Sallah: Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano Ta Sanya Sabbin Ka’idoji Kan Adaidaita Sahu, DJ Da Gidajen Wasanni

Daga: Muhammad Adamu Abubakar  Hukumar Tace Fina-Finai da Dabi’u ta Jihar Kano ta…

Da Dumi-Dumi: Ƙaramin Ministan Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Rage Talauci Ya Yi Murabus

Ƙaramin Ministan Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Dr. Yusuf Tanko…

Murtala Garo Ya Yabawa Hafiz Abubakar, Ya Nemi Shawarwari Domin Cigaban Kano

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo,…