Daga: Ibrahim Sani Gama

Mutane 176 da aka sace a hare-haren da ‘yan ta’adda suka kai kauyukan Woro da Nuku da ke Ƙaramar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara a ranar 3 ga Fabrairun shekarar nan, sun samu ‘yanci bayan sun shafe kusan wata shida a hannun masu garkuwa da su.

Gwamnatin Jihar Kwara ta tabbatar da sakin mutanen, inda ta yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki kan rawar da suka taka wajen ganin an kubutar da su.

Yawancin wadanda aka sace mata da kananan yara ne. Sun shiga hannun ‘yan ta’addar ne bayan mamayar da aka kai wa kauyukan na Woro da Nuku, inda aka kashe mutane da dama tare da kona gidaje.

Har zuwa lokacin fitar da wannan rahoto, ba a bayyana yadda aka samu sakin mutanen ba, kuma ba a tabbatar ko an biya kudin fansa ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Hukumar karota zata gayyato hukumar Yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi domin tantance jami ‘anta

Shugaban Hukumar Karota a Jihar Kano Alhaji Faisal Mahmud Kabir, ya bayyana…

Direbobin NURTW Tashar Malam Kato Sun Yi Jimamin Rasa Babban Jigo A Kano

Daga: Ibrahim Sani Gama Kungiyar matuka motocin haya ta kasa reshen tashar malam…

Gidauniyoyi Sun Ceto Wasu Yara Dake Tituna a Kano, Sun Saka Su Cikin Farin Ciki

Daga: Saminu Ibrahim Magashi A wani mataki na nuna jinkai da kula da…

Ali Dalori: Ya Karɓi Ragamar APC Na Ƙasa, Ya Yi Alkawarin Ƙarfafa Haɗin Kai Da Jagoranci Na Gaskiya

Daga: Hamza Garba Yakasai Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar APC na ƙasa,…