Daga: Musa Mudi Dawakin Tofa

Malam Ali Yakubu Danjumma ne ya baiyana haka yayin gabatar da nasiha a kan muhimmacin taimakon maraya, wanda kungiyar tsoffin daliban makarantar Firamaren Dawakin Tofa aji na shekara ta alif 1992, da ta gudanar a shekara ta 2025.

Malam Yakubu Danjuma, ya ce akwai misalin hadisi dake baiyana cewa duk wanda ya taimaki maraya zai yi makwabtaka ta kurkusa da Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama, a gidan Aljanna.

Talban Alajawa Alhaji Ibrahim Yaro Dawakin Tofa, ya yi kira ga abokan karatu da su rika bada tallafinsu a duk lokacin da za’a tallafawa rayuwar marayu dama mabukata, saboda hannun karba ya fi hannun bayarwa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa an rabawa yara marayu maza da mata tufafin Shaddoji da Atamfofi don sanya musu farin ciki, a sakamakon sun rasa iyayensu maza tun suna marhalar yarinta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Masu Buƙata Ta Musamman A Kano Sun Koka Kan Rashin Samun Tallafin Gwamnati

Daga: Ibrahim Sani Gama Shugabancin Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa Masu Buƙata ta Musamman ta…

An ja Hankalin Mata Dasu Tashi Tsaye Wajen Neman Abinda Zasu Dogara da Kansu – Hajiya Umma Sulaiman ‘Yan’Awaki

Daga: Sani Idris Maiwaya An ja Hankalin Mata Dasu Tashi Tsaye Wajen…

YABO DA KIRA: Shugaban APC na Giginyu Ya Jinjinawa Gwamna Abba, Ya Nemi A Gyara Gadar Badawa

Daga: Ibrahim Sani Gama Shugaban ƙungiyar Giginyu Peace kuma Shugaban jam’iyyar APC na…

Gwamnatin Tarayya Ta Dauki Matakin Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Daga: Sani Ibrahim Gama Gwamnatin tarayya ta shiga tsakani don warware rikicin…