Daga: Shehu Suleiman Sharfadi

Gwamnatin jihar Kano a hukumance ta kaddamar da jigilar alhazai na farko na aikin hajjin 2025 zuwa kasar Saudiyya.

Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam Gwarzo, wanda ya wakilci Gwamnan Jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jaddada aniyar gwamnatin na ganin an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya kuma kara da cewa gwamnatin jihar ta shirya tsaf domin kare jin dadin alhazanta da suka hada da samar da wurin kwana, ciyarwa, da tallafi na gaba daya a duk lokacin da suke gudanar da ayyukansu.

Ya yi nuni da cewa gwamnatin jihar ta yi tsayuwar daka wajen kiyaye jin dadin alhazanta da suka hada da samar da masauki, ciyarwa, da tallafi na gaba daya.

Mataimakin Gwamnan Kano Kwamared Gwarzo ya bukaci maniyyatan da su kasance masu da’a, hakuri, da mutuntawa, inda ya karfafa musu gwiwar zama jakadu nagari na jihar Kano da Najeriya baki daya.

Wakilinmu na ofishin mataimakin gwamna ya ruwaito cewar taron kaddamar da tuta ya samu halartar Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Mai Martaba Muhammadu Sanusi II, da ‘yan majalisar zartarwa ta jiha, da shugabannin kananan hukumomi, da sauran manyan baki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Sallah: Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano Ta Sanya Sabbin Ka’idoji Kan Adaidaita Sahu, DJ Da Gidajen Wasanni

Daga: Muhammad Adamu Abubakar  Hukumar Tace Fina-Finai da Dabi’u ta Jihar Kano ta…

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Ya Kai Ziyarar Jajantawa Asibitin Malam Aminu Kano

Daga: Shehu Suleiman sharfadi Mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo,…

A Shirye Muke Mu Yi Aiki da Kungiyar Matan 12 Pillars – Hon. Surajo Imam

Daga: Sani Idris Maiwaya DALA, KANO – Shugaban Karamar Hukumar Dala, Alhaji Surajo…

Muna Bukatar Gwamnati Ta Samar Mana Wurin Tsayawa Na Din Din Din – Giredi

Daga: Ibrahim Sani Gama Shugabancin kungiyar matuka motocin haya ta kasa reshen…