Daga: Mas’ud Mato Garo
Mataimakin gwamnan kanon ya bayyana hakan ne yayin da yake wakiltar Gwamna Abba Kabir Yusuf a taron bita kan aiwatar da dokar kare bayanai, wanda Ƙungiyar Gwamnoni ta Ƙasa (NGF) ta shirya tare da Hukumar Kare Bayanan ‘Yan Ƙasa (NDPC) a Abuja.
Alhaji Murtala Sule Garo ya jaddada cewa bayanan al’umma na daga cikin muhimman abubuwa da gwamnati ke bukata wajen tsara manufofin ci gaba, don haka akwai bukatar ba su cikakkiyar kariya a koda yaushe.

Ya kara da cewa kare bayanan na ’yan ƙasa nauyi ne na kowa, inda ya buƙaci jami’an gwamnati su kula da tsaron bayanan jama’a tare da kiran gwamnatoci su riƙa shirya tarukan horas da ma’aikata a kai a kai.
A yayin taron, Mataimakin Gwamnan na tare da Babban Daraktan Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Jihar Kano (KASITDA), Dr Bashir Muzzakkar, da Mai Ba Gwamna Shawara kan Tattalin Arzikin Zamani, Malam Yusuf Ibrahim Sharada, da sauran wakilan jihar Kano.