Daga: Mas’ud Mato Garo

Mataimakin gwamnan kanon ya bayyana hakan ne yayin da yake wakiltar Gwamna Abba Kabir Yusuf a taron bita kan aiwatar da dokar kare bayanai, wanda Ƙungiyar Gwamnoni ta Ƙasa (NGF) ta shirya tare da Hukumar Kare Bayanan ‘Yan Ƙasa (NDPC) a Abuja.

Alhaji Murtala Sule Garo ya jaddada cewa bayanan al’umma na daga cikin muhimman abubuwa da gwamnati ke bukata wajen tsara manufofin ci gaba, don haka akwai bukatar ba su cikakkiyar kariya a koda yaushe.

Ya kara da cewa kare bayanan na ’yan ƙasa nauyi ne na kowa, inda ya buƙaci jami’an gwamnati su kula da tsaron bayanan jama’a tare da kiran gwamnatoci su riƙa shirya tarukan horas da ma’aikata a kai a kai.

A yayin taron, Mataimakin Gwamnan na tare da Babban Daraktan Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Jihar Kano (KASITDA), Dr Bashir Muzzakkar, da Mai Ba Gwamna Shawara kan Tattalin Arzikin Zamani, Malam Yusuf Ibrahim Sharada, da sauran wakilan jihar Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Shugabannin Majalisa Sun Nuna Fargaba Kan Tsananin Ciwo Bashi da Rashin Sa Ido

Daga: Ibrahim Sani Gama Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, tare da Shugaban…

Yobe Ta Ware Naira Miliyan 460.8 Domin Tallafa Wa Mata Masu Sana’ar Kosai Da Sauransu

Daga: Ibrahim Sani Gama  Gwamnatin Jihar Yobe ta amince da kashe Naira…

An Kama Jabun Magunguna Na Naira Biliyan 1.3 a Kano

Daga: Ibrahim Sani Gama  Gwamnatin Jihar Kano ta samu gagarumar nasara a…

Ya Zama wajibi su Girbi Abinda Suka Shuka a Karamar Hukumar Ungogo…. Nuhu Musa Muhammad Kunture

Daga: Sani Idris Maiwaya Nuhu Musa Muhammad. Dan Kishin Al’umma. Lokaci ya…