By: Mukhtar Yahaya Shehu

A ranar Litinin, 23 ga Maris, 2026, Darakta Janar na Hukumar Kula da Lafiya na Matakin Farko ta Jihar Kano Professor Salisu Ahmad Ibrahim, ya kai ziyara ta gaggawa a Cibiyar lafiya ta Farko da ke Kabuga  (PHC) domin duba ayyukan ma’aikata da inganta ingancin kula da lafiya a fadin jihar Kano.

A cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a wato Sa’adatu Sulaiman ta saka hannu, Darakta Janar ya nuna damuwa kan rashin zuwan ma’aikata aiki da kuma rashin kiyaye lokutan aiki, wanda hakan ke kawo cikas ga ingantaccen aikin ta hukumar dake Kabuga.

A matsayin mataki na gaggawa don dawo da oda da inganci, Professor Ibrahim ya sauke mukamin mataimakiyar jami’ar cibiyar daga aiki, inda ya nada Khadija T. Musa a madadinta wadda aka bayyana da jajircewa da kiyaye lokaci.

Haka kuma, sashen Rigakafin Yara (Routine Immunization – RI Unit) ya samu sabon tsarin shugabanci bayan an gano matsalolin gudanarwa. An maye gurbin jami’in sashen da Maimuna Adnan Abdulhamid domin tabbatar da kyakkyawar hadin kai da karfafa ayyukan rigakafi a cibiyar.

Bugu da kari, an bai wa sauran ma’aikatan cibiyar takardun gargaɗi kan rashin bin lokutan aiki. Professor Ibrahim ya sake jaddada tsananin hukunci kan rashin ladabi, tare da bayyana muhimmancin ladabi, himma, da kwarewa wajen bayar da ingantaccen kulawa ga lafiyar al’ummar jihar Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Iftar: Gwamnatin Kano Ba Za Ta Lamunci Cin Zarafi A Kafafen Yada Labarai Ba – Comrade Waiya

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu Gwamnatin jihar Kano ta yi alwashin hada hannu da…

Kungiyar Matasa Masu Neman Aikin Koyarwa Ta Yabawa Gwamnatin Kano Kan Tsarin Jarabawa

Daga: Ibrahim Sani Gama Kungiyar matasan da suka rubuta jarrabawar neman aikin koyarwa…

Gwamnatin Kano Na Cigaba Da Yiwa Ilimi Gata Don Kyautata Rayuwar Al’umma – Hon. Rabiu

Daga: Kabir Getso Gwamnatin Kano na ciga ba da yiwa ilimi gata…

Sanarwa Ga Al’umma Musulmi: Duban Jinjirin Watan Muharram 1447AH

Daga: Sani Bagwai Wannan sanarwa ce ga al’ummar Musulmi cewa ranar Laraba, 25…