Daga: Mas’ud Mato Garo

Mataimakin gwamnan kanon ya bayyana hakan ne yayin da yake wakiltar Gwamna Abba Kabir Yusuf a taron bita kan aiwatar da dokar kare bayanai, wanda Ƙungiyar Gwamnoni ta Ƙasa (NGF) ta shirya tare da Hukumar Kare Bayanan ‘Yan Ƙasa (NDPC) a Abuja.

Alhaji Murtala Sule Garo ya jaddada cewa bayanan al’umma na daga cikin muhimman abubuwa da gwamnati ke bukata wajen tsara manufofin ci gaba, don haka akwai bukatar ba su cikakkiyar kariya a koda yaushe.

Ya kara da cewa kare bayanan na ’yan ƙasa nauyi ne na kowa, inda ya buƙaci jami’an gwamnati su kula da tsaron bayanan jama’a tare da kiran gwamnatoci su riƙa shirya tarukan horas da ma’aikata a kai a kai.

A yayin taron, Mataimakin Gwamnan na tare da Babban Daraktan Hukumar Bunkasa Fasahar Sadarwa ta Jihar Kano (KASITDA), Dr Bashir Muzzakkar, da Mai Ba Gwamna Shawara kan Tattalin Arzikin Zamani, Malam Yusuf Ibrahim Sharada, da sauran wakilan jihar Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Iyaye Kan Illar Auren Dole

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Gwamnatin jihar Kano ta gargadi iyaye maza da mata…

Kwalejin Audu Bako Ta Karyata Zargin Kin Bin Umarnin Gwamnatin Jihar Kano

Daga: Kabiru Getso Shugaban Kwalejin koyar da aikin gona ta Audu Bako da…

Zulum Ya Ware N12.9bn Don Daukar Nauyin Dalibai 54 ’Yan Borno A Fannin Jiragen Sama Da Injiniyoyi

Daga: Kabir Getso Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da…

Hajj 2027: Hukumar Jin Dadin Alhazan Kano Ta Gargadi Ga Maniyyata Kan Mika Passport Kan Lokaci – DG

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu  Hukumar Jin Dadin Alhazan jihar Kano tana kara gargadin…