Daga: Sani Muhammad 

Kungiyar Masu Karɓar Fansho ta Najeriya ta ce an kafa ta ne domin kare jin daɗi da walwalar ‘yan fansho, da kuma tabbatar da cewa sun samu haƙƙoƙinsu.

Shugaban reshen ƙungiyar na Jihar Kano, Kwamared Shu’aibu Musa Jibril, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da manema labarai a Kano.

Ya ce shugabannin da suka gabata sun bayar da gagarumar gudummawa wajen bunƙasa da inganta tsarin fansho.

A cewarsa, manufar kafa ƙungiyar ita ce tabbatar da cewa ‘yan fansho sun samu alawus-alawus da sauran haƙƙoƙin da suka cancanta.

Kwamared Shu’aibu ya yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin ‘yan fansho, tare da tabbatar da biyan kuɗaɗen fansho cikin lokaci.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

An Kama Jabun Magunguna Na Naira Biliyan 1.3 a Kano

Daga: Ibrahim Sani Gama  Gwamnatin Jihar Kano ta samu gagarumar nasara a…

Mawuyacin Halin Da Makarantun Firamare Da Sakandire Na Langel A Ƙaramar Hukumar Tofa Ke Ciki

Daga:  Aliyu Ahmad Makarantun firamare da sakandire da ke ƙauyen Langel a…

Gwamna Abba Ya Yabawa Ganduje Bayan Musuluntar Da Mutane 370 A Kano

Daga: Mas’ud Mato Garo  Gwamnan jihar kano Alh Abba Kabir Yusuf, ya…

Cigaba Da Ayyukan Alheri Bayan Ramadan Alama Ce Ta Karɓuwar Ibadar Bawa — Sheikh Kamalu Inuwa

Daga: Abdulmajid Habib Tukuntawa Cigaba da aikata kyawawan ayyuka bayan watan Ramadan na…