Daga: Ibrahim Sani Gama

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa kiran waya da ya yi masa tare da taya shi murnar samun nasara a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar jiya Asabar.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan samun ƙuri’u 511,067, inda ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, ya samu ƙuri’u 444,815.

Adeleke, yayin da yake magana bayan sanar da sakamakon zaɓen, ya bayyana nasarar a matsayin cikakkiyar dimokuraɗiyya ga al’ummar Osun.

Ya ce: “Ina amfani da wannan dama wajen gode wa Mai Girma Shugaban Ƙasa. Shugaban Ƙasa ya kira ni ya taya ni murna. Na godewa, Shugaban Ƙasa, saboda tabbatar da cewa dimokuraɗiyya ta ci gaba da wanzuwa.”

Gwamnan ya kuma bayyana cewa nasarar tasa ta nuna amincewar al’ummar jihar da ayyukan gwamnatinsa, musamman a fannonin samar da ababen more rayuwa, kiwon lafiya da tsaro.

Adeleke ya samu nasara a ƙananan hukumomi 19 daga cikin 30 na jihar, yayin da Oyebamiji ya samu nasara a ƙananan hukumomi 11, abin da ya bai wa gwamnan tazarar ƙuri’u 66,252.

Haka kuma, Adeleke ya yi kira da a duba zaɓen a matsayin nasara ga kowa, yana mai cewa babu wanda ya yi rashin nasara, kuma yana fatan abokin hamayyarsa zai kira shi domin taya shi murna.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Matar Marigayi Buhari Ta Ziyarci Atiku A Saudiyya

Matar marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, ta kai ziyara ga tsohon…

Gwamnatin Jihar Kano Ta Jajantawa Iyalan ‘Yan Wasan Motsa Jiki Da Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Dasu

  Daga: Shehu Suleiman Sharfadi  Gwamnatin jihar Kano ta sanar da bayar…

Gwamnatin Jihar Kano Ta Jaddada Aniyarta Na Tallafawa Ilimi A Kan Manufofin Zamani

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Gwamnatin jihar Kano ta jaddada sadaukar da kai…

CSI T. Sa’eed Ya Sake Bada Kyautarsa Ga Hazikan Dalibai A S.P.S. Dawakin Tofa

Daga: Musa Mudi Dawakin Tofa A kokarinsa na kara zaburar da dalibai…