Daga: Saminu Ibrahim Magashi
Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya yaba wa ƙoƙarin ƙungiyar tsofaffin ɗaliban Makarantar Kano Capital wajen farfaɗo da martabar makarantar da kuma tallafa mata domin ci gaban harkar ilimi.
Da yake jawabi a yayin bikin cikar Makarantar Kano Capital shekaru 35 da kafuwa, Sarkin Kano ya bayyana ilimi a matsayin muhimmiyar hanya ta kawo gyara a cikin al’amuran rayuwa. Ya kuma yi alƙawarin haɗa kai da masu ruwa da tsaki domin ganin an dawo da martabar makarantar kamar yadda take a baya.
A nata jawabin, shugabar kwamitin shirya taron, Barrister Faiza Dahiru Sidi, ta ce manufar shirya taron ita ce duba halin da makarantar ke ciki, musamman yadda ta koma baya, tare da tattaro tsofaffin ɗaliban makarantar domin kawo mata agajin gaggawa.
Ta ƙara kira ga tsofaffin ɗaliban da su ci gaba da ba makarantar cikakken goyon baya domin samun damar inganta yanayin karatu da koyarwa.
Haka kuma, Dr. Surayya Ado Bala ta bayyana cewa ƙungiyar ta tallafa wa makarantar da teburan zama guda 150 da allunan rubutu guda shida, tare da gyaran bandakuna. Ta ce an kuma tallafa wa ƙananan ma’aikatan makarantar da kuɗi da kayan abinci.

Ita ma shugabar sashen mata na Makarantar Kano Capital ta nuna matuƙar godiya ga tsofaffin ɗaliban bisa irin tallafin da suka bayar, tana mai cewa ba kasafai ake samun irin wannan haɗin kai da taimako ba.
Ta ƙara da cewa tsofaffin ɗaliban sun yi alƙawarin yin duk mai yiwuwa wajen ganin makarantar ta dawo hayyacinta da martabarta ta baya.
Shugabar ta kuma yaba wa ƙoƙarin Gwamnatin Jihar Kano wajen tallafawa harkar ilimi da kuma ƙoƙarin inganta fannin ilimi a jihar.