Daga: Ibrahim Sani Gama

Hukumar NAFDAC reshen jihar Kano ta cafke mutane shida tare da rufe wasu shaguna a kasuwar Sabon Gari, sakamakon kama da su da laifin sayar da man gyaran fata da ba shi da sahalewar hukuma.

Shugaban hukumar a jihar, Kasim Ibrahim, ya bayyana wa manema labarai a ranar Talata cewa matakin ya biyo bayan korafe-korafen da jama’a suka shigar ta kafafen sada zumunta, wanda hakan ya janyo umarnin bincike daga shugabar hukumar ta ƙasa.

“A sakamakon korafe-korafen da muka samu, sai muka fara bincike cikin sirri, har ma muka sayi wasu daga cikin kayayyakin da ake zargin don tabbatar da ingancinsu,” in ji Ibrahim.

Binciken ya gano mutane shida da ake zargin suna da hannu wajen rarrabawa da amfani da man ba bisa ƙa’ida ba.

Ibrahim ya ƙara da cewa mayukan da aka kama na kama da kayan kwalliya ne, amma suna ɗauke da sinadarai masu haɗari waɗanda NAFDAC ba ta amince da su ba.

Tare da haɗin guiwar sashen bincike da aiwatar da dokoki na NAFDAC, an kama waɗanda ake zargi, an rufe shagunansu, sannan an dauki samfurin man domin gwajin dakin bincike.

Bugu da ƙari, an kuma rufe wasu kamfanonin da ke kwaikwayon kayayyakin da aka riga aka yi wa rajista, ko kuma suka karya ka’idojin hukumar, har sai an kammala bincike.

Ibrahim ya bukaci jama’a da su kasance masu lura da kayayyakin da ake sayarwa, su kuma rika sanar da NAFDAC idan suka gano wani abu da ya saba wa doka.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Falgore Ya Taya Musulmai Murnar Sabuwar Shekarar Muslunci, Ya Kuma Tabbatar da Kudurin Majalisa Kan Samar da Dokoki Masu Inganci a Kano

Daga: Muhammad Adamu Abubakar  Biyo bayan ayyana yau Alhamis, 26 ga watan Yunin…

Gwamnatin Kano Ta Shirya Gina Goben Masu Bukata Ta Musamman

Daga: Jamila Suleiman Aliyu  Gwamnatin Kano ta sha alwashin marawa matasa, masu bukata…

An Bukaci Gwamnati Ta Ƙirƙiri Kwamitin Kar-ta-Kwana Kan Daukar Fasinjoji a Kan Tituna

Daga: Ibrahim Sani Gama Kungiyar matuka motocin haya ta kasa reshen jihar…

Bayan Shafe Wata Shida A Hannun ‘Yan Ta’adda, Mutane 176 Sun Shaki Iskar ‘Yanci A Jihar Kwara

Daga: Ibrahim Sani Gama Mutane 176 da aka sace a hare-haren da ‘yan…