Daga: Mukhtar Yahaya Shehu 

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr Nasiru Yusuf Gawuna ya bi sahun Al’uma bisa ziyarar Ta’aziyya Unguwar Dorayi Chiranci ga mutumin da aka kashe wa matar sa da ‘ya ‘yan sa 6.

Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya yin ziyarar ta’aziyyar ga wannan mutumin wato Malam Haruna ya bayyana takaici tare da jimamin wannan lamari.

Tsohon mataimakin gwamnan Wanda kuma shi ne shugaban karamar Gudanarwar Bankin bayar da lamunin gidaje na kasa ya yi addu’ar Allah Ya karbi Shahadar su tare da bai wa Malam Haruna hakurin wannan babban rashi.

Cikin sanarwa mai dauke da sa hannun mai taimaka masa ta fannin yada Labarai Abubakar Musa DK Dr. Gawuna ya kuma yi addu’ar Allah ya kare afkuwar hakan a nan gaba. Ya kuma cigaba da bai wa jihar Kano da ma kasa baki daya zaman lafiya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Sakkwato: Ba Za’a Yi Sulhu Da Turji Ba Sai Ya Sako Wadanda Ya Yi Garkuwa Da Su

Daga: Sani Idris Maiwaya Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bukaci shugaban ’yan bindiga, Bello…

Kungiyar Kwankwasiyya Kasuwar Singa Ta Nemi Tallafin Jari Daga Gwamnatin Kano

Daga: Ibrahim Sani Gama Kungiyar ‘yan kasuwar kayayyakin masarufi ta kasa, reshen…

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Dakile Satar Fasaha a Fannin Buga Littattafai

Daga: Ibrahim Sani Gama Gwamnatin Tarayya ta jaddada kudirinta na kawo karshen satar…

Jami’an Gwamnati Daga Bangarori Daban-Daban Na Kawo Ziyarar Ta’aziyya Gwamnatin Kano

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Biyo bayan rasuwar ‘yan wasan Kano 22 da…