Daga: Sani Muhammad
Kungiyar Masu Karɓar Fansho ta Najeriya ta ce an kafa ta ne domin kare jin daɗi da walwalar ‘yan fansho, da kuma tabbatar da cewa sun samu haƙƙoƙinsu.
Shugaban reshen ƙungiyar na Jihar Kano, Kwamared Shu’aibu Musa Jibril, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da manema labarai a Kano.

Ya ce shugabannin da suka gabata sun bayar da gagarumar gudummawa wajen bunƙasa da inganta tsarin fansho.
A cewarsa, manufar kafa ƙungiyar ita ce tabbatar da cewa ‘yan fansho sun samu alawus-alawus da sauran haƙƙoƙin da suka cancanta.
Kwamared Shu’aibu ya yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin ‘yan fansho, tare da tabbatar da biyan kuɗaɗen fansho cikin lokaci.