Daga: Sani Muhammad 

Kungiyar Masu Karɓar Fansho ta Najeriya ta ce an kafa ta ne domin kare jin daɗi da walwalar ‘yan fansho, da kuma tabbatar da cewa sun samu haƙƙoƙinsu.

Shugaban reshen ƙungiyar na Jihar Kano, Kwamared Shu’aibu Musa Jibril, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da manema labarai a Kano.

Ya ce shugabannin da suka gabata sun bayar da gagarumar gudummawa wajen bunƙasa da inganta tsarin fansho.

A cewarsa, manufar kafa ƙungiyar ita ce tabbatar da cewa ‘yan fansho sun samu alawus-alawus da sauran haƙƙoƙin da suka cancanta.

Kwamared Shu’aibu ya yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin ‘yan fansho, tare da tabbatar da biyan kuɗaɗen fansho cikin lokaci.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

2027: APC Ta Tsayar da Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu

Daga: Ibrahim Sani Gama Jam’iyyar APC ta tabbatar da ci gaba da…

An Ƙaddamar Da Hukumar Asusun Tsaron Arewa

Daga: Abdullahi Bashir Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewacin Najeriya ta kafa Hukumar Asusun…

Matasan Rimin Gado Sun Zargi Barau Da Siyen Kuri’a, Sun Bukaci Gaskiyar Tallafi

Daga: Ibrahim Sani Gama Shugaban kungiyar matasan ‘yan siyasa a karamar hukumar Rimin…

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano, Gawuna, Ya Sauya Jam’iyya

Daga: Hamza Musa Yakasai Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Nasir Yusuf Gawuna, ya…