Daga: Ibrahim Sani Gama
Shugaban kungiyar matasan ‘yan siyasa a karamar hukumar Rimin Gado ya bukaci Sanata Barau I. Jibrin da ya mayar da hankali wajen tallafawa al’ummar mazabarsa ba tare da jiran lokacin zabe ba.

Shugaban kungiyar, Aminu Abdullahi Sidi (Juji), ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai. Ya ce matasan yankin na ganin cewa rabon kudi da ake yi a lokacin siyasa ba ya wakiltar ingantaccen tallafi, yana mai cewa “masoya na gaskiya ba a sayensu da kudi.”

Ya zargi Sanatan da fito da wani tsari na tara mutane tare da raba musu kudi domin jawo hankalinsu gabanin zabe, yana mai cewa wannan hanya ba za ta haifar da nasara ba, domin al’umma sun fara fahimtar yadda ake tafiyar da siyasa.
A cewarsa, maimakon hakan, ya kamata Sanatan ya koma ga mutanen da suka mara masa baya tun farko, wadanda a cewarsa yanzu suna cikin halin kunci da talauci.

Kungiyar ta kuma bukaci duk wanda aka gayyata domin karbar irin wannan tallafi da ya karba a matsayin hakkinsa, amma ta gargadi jama’a da kada su yarda a yaudare su da irin wadannan dabaru na siyasa da ba su da dorewa.