Daga: Yakubu Abubakar Gwagwarwa 

Kwamishinan Sufuri na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Namadi, ya janye matsayin da ya dauka na tsayawa beli ga wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi a gaban kotu.

Sanarwar hakan na kunshe ne a wata takarda da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Abdullatif Auta, ya fitar a ranar Juma’a.

A cewar sanarwar, Kwamishina Namadi ya rubuta wa kotu wasika yana bayyana aniyarsa ta janye belin da ya tsaya wa Sulaiman Aminu Danwawu, wanda Hukumar NDLEA ke tuhuma da laifin safarar miyagun kwayoyi.

Kwamishinan ya ce ya dauki matakin janye belin ne saboda dalilai na kashin kai da kuma bukatar kare mutuncinsa da martabar ofishin da yake rike da shi.

Ya ce lokacin da ya tsaya wa Danwawu beli, ya yi hakan ne saboda alakar jini da ke tsakaninsu da kuma jin kai, amma ba saboda yana marawa baya ayyukan da ake tuhuma da su ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Tarayya Ta Dauki Matakin Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Daga: Sani Ibrahim Gama Gwamnatin tarayya ta shiga tsakani don warware rikicin…

Ganawar Al’ummar D/Kudu da Kwankwaso: Har Yanzu Shi Ke Da Jama’ar Kano – Hon. Abdulmumin Tijjani Mai POS

Daga: Kabir Getso Tsohon ɗan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Dala/Kudu…

Tarihi, Gwagwarmayar Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari Da Ya Rasu A Birtaniya

Daga: Sani Idris Maiwaya A cikin wani babban rashi da ya girgiza…

Tinubu Zai Yi Wa Shugabannin Duniya Jawabi A Taron MDD Na 81

Daga: Abdullahi Bashir Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gabatar da jawabi a gaban…