Daga: Kabir Getso
Tsohon ɗan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Dala/Kudu da Warawa, Hon. Abdulmuminu Tijjani (Mai POS), ya bayyana cewa taron da al’ummar ƙaramar hukumar Dala/Kudu suka kai wa Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso a gidansa da ke Miller Road ya nuna irin goyon bayan da jagoran ke da shi a Jihar Kano.

Hon. Mai POS ya ce ya yi matuƙar mamaki da yawan jama’ar da suka halarci ganawar, yana mai cewa hakan wata alama ce ta irin ƙaunar da magoya baya ke nunawa ga Kwankwaso.
Da yake tsokaci kan rahotannin sauyin jam’iyya da ake dangantawa da Gwamnan Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, Hon. Mai POS ya ce mutane da dama na bayyana mamaki kan matakan siyasar da ake samu a jihar, amma ya jaddada cewa, a cewarsa, goyon bayan da Kwankwaso ke da shi a tsakanin al’umma ba zai sauya cikin sauƙi ba.

Ya ƙara da cewa a zaɓukan baya, a cewarsa, yawancin magoya bayan jam’iyyar sun fi mayar da hankali kan jagorancin Kwankwaso, yana mai cewa wannan ne ya sa yake ganin tafiyar Kwankwasiyya za ta ci gaba da ƙarfi.
Haka kuma, ya ce duk waɗanda ke tare da gwamnati a halin yanzu suna da damar ci gaba da tafiyarsu, amma ya yi hasashen cewa wasu na iya sauya matsayi a nan gaba.
Hon. Mai POS ya bayyana taron a matsayin wata alama da ke nuna yadda magoya baya a sassa daban-daban na Kano ke ci gaba da nuna goyon baya ga jagoran, tare da kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da haƙuri da biyayya, yana mai cewa suna sa ran samun sauye-sauye masu kyau a nan gaba.
