Daga: Garba Hamza Yakasai

Tsohon gwamnan jihar Sokoto State kuma Sanata mai wakiltar Sokoto South Senatorial District, Aminu Waziri Tambuwal, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a hukumance.

Tambuwal ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 11 ga Maris, 2026, wadda ya aikawa shugaban jam’iyyar PDP na mazabarsa, inda ya ce ya fice daga jam’iyyar nan take.

Sanatan ya kuma sanar da cewa shi da magoya bayansa sun shiga jam’iyyar ADC, yana mai jaddada cewa ya ɗauki matakin ne bisa imaninsa cewa Nigeria na buƙatar tsarin siyasa mai ƙarfi da ya ginu kan gaskiya, riƙon amana da haɗin kai, domin samar da ingantaccen ci gaba ga ƙasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Wata Gidauniya Ta Nemi Haɗin Gwiwa Da Ma’aikatar Jin Ƙai Domin Ciyarwar Watan Ramadan

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu  Gidauniyar Save Yateem Orphans ta bayyana aniyarta ta yin…

Gasar Kofin Tsofaffin ‘Yan Wasan Kwallo Na Kara Zaman Lafiya da Haɗin Kai a Cikin Ƙasa – Inji Hon. Danburan

Daga: Zaharadeen Saleh  Shugaban ƙungiyar shirya gasar tsofaffin ‘yan wasan ƙwallon ƙafa…

Kungiyar kwankwasiyya singa market ta yabawa Gwamnan jihar Kano injiniya Abba Kabir Yusuf,bisa gudunmawar da ya bayar a kasa maitsarki

Daga: Ibrahim Sani Gama    Kungiyar kwankwasiyya singa market dake nan jihar…

Wannan nadin da Gwamnan Kano yayiwa Shiek Bazallahi ko Kusa bai Shafi mukamin da Abba El-Mustapha Ke kaiba na Babban Sakataren Hukumar