Daga: Ibrahim Sani Gama

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana al’ummar Hausawa a matsayin manyan ginshiƙai wajen tabbatar da haɗin kan Najeriya da ci gabanta.

Shugaban ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a yau Laraba, yayin da ake gudanar da bikin Ranar Hausa ta Duniya a fadar Mai Martaba Sarkin Daura, a Katsina.

Tinubu ya ce harshen Hausa ya samu gagarumin yaɗuwa, inda ya zama ɗaya daga cikin muhimman harsunan da ke taka rawa wajen haɗa kan al’umma da bunƙasa harkokin kasuwanci a Najeriya da sauran sassan duniya.

A cewar Shugaban Ƙasar, bikin Ranar Hausa wata dama ce ta nuna muhimmancin harshen da al’adun Hausawa wajen haɓaka haɗin kai da fahimtar juna tsakanin al’ummomin Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Hausawa murnar Ranar Hausa, wadda ake gudanar da bikin ta a yau a fadar Daura mai tarihi,” in ji shi.

Ana bikin Ranar Hausa ta Duniya, wato Ranar Hausa, a duk ranar 26 ga watan Agusta na kowace shekara, domin tunawa da muhimmancin harshen Hausa da kuma irin gudunmawar da yake bayarwa wajen sadarwa da adana al’adu.

Harshen Hausa na daga cikin manyan harsunan da ake magana da su a Najeriya, kuma yana daga cikin harsunan da suka fi yaɗuwa a nahiyar Afirka.

Masana sun bayyana Hausa a matsayin ɗaya daga cikin muhimman harsunan Afirka, wanda ake amfani da shi wajen sadarwa, ilimi, kafafen yaɗa labarai da harkokin kasuwanci a sassa da dama na nahiyar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Kasa Ya Taya Gwamnatin Kano Alhinin Rasuwar ‘Yan Wasanninta

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Biyo bayan rasuwar ‘yan wasan Kano 22 da…

Kungiyar Agajin Musulmi Za Ta Haɗa Gwiwa da Ma’aikatar Jinƙai Don Tallafa wa Mabuƙata

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu  Kwamishinan Ma’aikatar Jin Кai da Rage Talauci ta jihar…

Yakin Amurka/Isra’ila Da Iran: Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-Zanga A Baghdad

Daga: Abdullahi Bashir Jami’an tsaro a birnin Baghdaza sun yi amfani da…

Fashewar Tankar Mai A Jihar Neja Wadanda Suka Rasu Sun Karu Zuwa 39 Inda 60 Suka Jikkata – NEMA

Daga: Kabir Getso Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta tabbatar da…