Daga: Abdullahi Bashir

Babban Ministan Kudi na ƙasa, Wale Edun, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ba za ta tsoma baki wajen kayyade farashin fetur ba duk da tashin hankali da ake fama da shi a yankin Gabas ta Tsakiya wanda ke janyo sauyin farashin mai a kasuwannin duniya.

Edun ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Gidan Telebijin din Channels a daren jiya Laraba.

Ya ce maimakon gwamnatin ta kayyade farashin fetur, tana shirin bullo da wasu tsare-tsare da za su taimaka wajen rage tasirin yakin kan siyasar duniya na tattalin arzikin Najeriya da rayuwar al’umma.

Ministan ya ƙara da cewa, tuni Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da samar da ƙarin kayan sauya motoci zuwa amfani da iskar Gas guda 100,000 domin bai wa masu motoci damar komawa amfani da iskar Gas din.

A cewarsa, amfani da CNG yana da araha sosai, domin farashinsa yana tsakanin kashi 25 zuwa 30 cikin 100 na farashin fetur, abin da ake sa ran zai taimaka wajen rage kuɗin sufuri da kuma sauƙaƙa wa jama’a nauyin hauhawar farashin mai.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Garo Ya Wakilci Gwamna Abba A Taron Gwamnonin Arewa Da Majalisar Sarakunan Gargajiya

Daga: Mas’ud Mato Garo Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo,…

Gwamnan Filato Ya Yi Wa Jama’a Jawabi Daga Cikin Tanki Bayan Hari

Daga: Abdullahi Bashir Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang, ya sanar da kafa dokar…

KAROTA MD SEEKS GOVERNMENT INTERVENTION OVER RECURRENT CONFRONTATIONS WITH SOME MILITARY PERSONNEL DURING TRAFFIC ENFORCEMENT

  KAROTA MD SEEKS GOVERNMENT INTERVENTION OVER RECURRENT CONFRONTATIONS WITH SOME MILITARY…

Dalilin Da Ya Sa Atiku Bai Halarci Taron G-100 Ba — ADC

Daga: Abdullahi Bashir Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana dalilin da…