Daga: Abdullahi Bashir
Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang, ya sanar da kafa dokar ta-ɓaci ta awanni 48 a Ƙaramar Hukumar Jos North, bayan wani mummunan hari da ya auku a Angwan Rukuba.

Gwamnan ya yi wannan jawabi ne yayin da ya kai ziyara wurin da lamarin ya faru, inda ya bayyana cewa matakin na nufin dawo da doka da oda a yankin.
Ya kuma bai wa mazauna jihar tabbacin cewa za a gudanar da cikakken bincike domin gano waɗanda suka aikata harin tare da gurfanar da su a gaban kuliya.
Haka zalika, Mutfwang ya ce gwamnatin jihar za ta ɗauki nauyin jinyar waɗanda suka jikkata, tare da shirya jana’iza mai kyau ga waɗanda suka rasu.