Daga; Abdullahi Bashir

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya sake lashe zaben gwamnan jihar, inda ya samu nasarar komawa kan kujerar na wa’adin karo na biyu.

Adeleke, dan takarar jam’iyyar Accord, ya samu kuri’u 511,067, yayin da babban abokin hamayyarsa na jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, ya samu kuri’u 444,815.

Dan takarar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Najeem Salaam, ya zo na uku da kuri’u 17,180.

Jami’in zaben na INEC, Farfesa Joshua Ogunwole, ne ya bayyana sakamakon zaben a cibiyar tattara sakamakon zabe da ke Osogbo, babban birnin jihar, a safiyar yau Lahadi.

Adeleke ya samu nasara a kananan hukumomi 19 daga cikin 30 na jihar, yayin da Oyebamiji na APC ya samu nasara a kananan hukumomi 11.

Wannan nasara ta bai wa Adeleke damar ci gaba da jagorantar Jihar Osun na karin wa’adin shekaru hudu a karo na biyu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Tarayya Ta Daga Kudin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000 Daga 2027

Daga: Abdullahi Muhammad Abuja — Gwamnatin Tarayya ta amince da karin kudin jarabawar…

Ta’aziyya: Rasuwar Galadima Babban Rashi Ne A Masarautar Kano- Sanka

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu An bayyana rasuwar marigayi Galadiman Kano Alhaji Abbas Sunusi…

Gwamnatin Jihar Lagos ta Fara yin Gwajin lafiya ga Maniyyata aikin hajjin bana na Shekara 2026

Gwamnatin Jihar Lagos ta Fara yin Gwajin lafiya ga Maniyyata aikin hajjin…

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Aniyarta Na Ciyar Da Al’adun Gargajiya Gaba

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi Gwamnatin Jihar Kano ta jaddada kudirinta na farfaɗo…