Daga: Abdulmajid Habib Tukuntawa 

Akalla mutane 750 ne suka ci gajiyar tallafin bada magani da duba marasa lafiya kyauta da Hon. Abdullahi Nasir Mai Kwano, mai neman takarar kujerar Majalisar Jiha a Karamar Hukumar Warawa karkashin jam’iyyar NDC, ya dauki nauyi.

Tallafin ya hada da duba masu lalurar ido da masu fama da cutar “dan dumi”, inda aka raba musu magunguna da kuma gilashi kyauta.

An tsara duba mutane 50 a kowacce mazaba cikin mazabu 15 da ke Karamar Hukumar Warawa, wanda hakan ya sa adadin wadanda suka amfana ya kai kimanin mutum 750.

Hon. Abdullahi Nasir Mai Kwano ya bayyana cewa ya gudanar da wannan aiki ne domin tallafawa al’umma da kuma rage musu wahalhalun rayuwa daidai gwargwadon abin da Allah Ya hore masa.

Wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin sun bayyana farin cikinsu tare da godewa Hon. Abdullahi Nasir Mai Kwano bisa wannan aikin alkhairi da ya gudanar musu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Tarayya Ta Daga Kudin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000 Daga 2027

Daga: Abdullahi Muhammad Abuja — Gwamnatin Tarayya ta amince da karin kudin jarabawar…

Kwamitin Hana Fadan Daba Da Kwacen Waya Sun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano

Daga: Ibrahim Sani Gama Janar Gambo Ahmed Mai Addau mai ritaya ya…

Kungiyar Agajin Musulmi Za Ta Haɗa Gwiwa da Ma’aikatar Jinƙai Don Tallafa wa Mabuƙata

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu  Kwamishinan Ma’aikatar Jin Кai da Rage Talauci ta jihar…

A Shirye Muke Mu Yi Aiki da Kungiyar Matan 12 Pillars – Hon. Surajo Imam

Daga: Sani Idris Maiwaya DALA, KANO – Shugaban Karamar Hukumar Dala, Alhaji Surajo…