Daga: Nura Garba Jibrin
Kungiyar ’Yan Kasuwa da Masu Safarar Ridi ta Ƙasa, reshen Jihar Kano, ta bayyana cewa, matsalar tsaro na ci gaba da zama babbar barazana ga noman ridi a Arewacin Najeriya.
y
Shugaban kungiyar a kasuwar Dawanau, Ibrahim Muhammad Dawanau, wanda aka fi sani da Danliti Y.Y, ya bayyana haka a hirarsa da wakilinmu.
Ya ce matsalolin tsaro da ke addabar jihohin Borno, Zamfara, Katsina, Sokoto da Yobe na iya jefa harkar noman ridi cikin matsanancin hali har ta kai ga durkushewa.
Ya yi nuni da cewa, baya ga barazanar tsaro, akwai kuma kalubalen rashin kayan aikin noma irin su taraktoci, ingantattun iri da magungunan kashe kwari, abin da ya kara dagula sha’anin manoma.
“Idan aka samar da taki na zamani a farashi mai sauki tare da taraktoci da ingantaccen iri da magungunan kashe kwari, wallahi ni kadai zan iya noma hekta 100, amma a halin yanzu ko hekta 30 ba zan iya nomawa ba,” in ji Danliti Y.Y.

Shugaban ya yi kira ga gwamnatin tarayya, jihohi da kananan hukumomi da su dauki gaggawar matakai domin ceton noman ridi wanda ya ce ke da muhimmanci wajen bunkasa tattalin arzikin kasar.
A nasa bangaren, mataimakin shugaban kungiyar, Babangida Mansur, ya jinjinawa gwamnatin Jihar Kano musamman kwamishinan kasuwanci bisa irin matakan da suke dauka domin inganta harkokin kasuwanci a kasuwar Dawanau.
Ya bayyana cewa akwai bukatar gwamnatin Kano ta kara mai da hankali wajen horar da ’yan kasuwa kan dabarun karɓar rance daga gwamnatin tarayya da kuma kungiyoyin duniya. A cewarsa, samar da jari ba tare da kudin ruwa ba zai taimaka matuka wajen bunkasa tattalin arzikin jihar, ƙara kudaden shiga da kuma samar da ayyukan yi.
Mansur ya kuma shawarci ’yan kasuwa da su haɗa kai wajen samo hanyoyin da za su inganta harkokinsu, tare da tabbatar da dorewar cigaban tattalin arzikin Arewa.
