Daga: Ibrahim Sani Gama
An yi kira ga Gwamnatin jihar Kano, Karamar hukumar Wudil da ‘Yan majalisar wakilai na jiha da Tarayya, da su kawowa al’ummar mazabar Lajawa daukin gaggawa domin gyara musu hanyar da ta tashi daga ‘Yan Audu zuwa garin Lajawa duba da lalacewar da hanyar tayi.

Shugaban kungiyar matasan yankin Mahamud Nuhu Lajawa ne yayi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a nan jihar Kano.
Shugaban kungiyar ya bayyana cewar, sun dade suna ta yin kiraye-kiraye ga mahukunta da su zo domin gyara musu hanyar saboda barazanar da suke fuskanta dangane da titin, amma har yanzu ba’a gyara ba.

Yace kungiyar matasan yankin ta taka gagarumar gudunmawa wajen ganin mahukunta sun kawo musu dauki wanda, ya ce kamar yadda suka janyo hankulan al’ummar yankunan suka zabi Gwamnatin to kamata yayi su ma a share musu hawayensu.
Shugaban ya bayyana cewar, har kunyar Alummar yankunansa yake saboda tabbacin da suka baiwa jama’a a yayin da Gwamnati karkashin jagorancin Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf suka yi.
Mahamud Nuhu Lajawa ya kara da cewa, yanzu lokaci yayi da za’a ramawa kura aniyarta na gagin an gyara wannan titi da ya zama kalubale ga al’ummar karamar hukumar Wudil.
Yace, yanzu haka al’ummar yankunan sun fara cewa, idan Gwamnatin ba ta gyara musu hanyar ba, ba za su kara zabar duk wani Dantakara ba tun da basa morar komai daga Gwamnatin da suka zaba ba.
Dan haka shugaban kungiyar matasan yankin yake kiraye-kirayen masu ruwa da tsaki su taimakawa wadannan al’umma domin ganin an samar da wani sabon titin da zai kwantarwa da al’ummar yankunan hankalu.
Mahamud Lajawa ya kara da cewa, mazabar sun kai mutane dubu goma sha biyu wadanda suke da kada kuri”ar da za su zubawa Gwamnatin a kakar zabe mai zuwa, inda yace basa so Gwamnatin jihar Kano mai ci ta rasa wannan kuri’u shi yasa kungiyar matasan yankin take ta yin kiran Gwamnati ta zo domin gyara wannan hanya.
Haka zalika shugaban kungiyar yace, ba za su fasa yin kiraye kirayen mahukunta su zo domin gyara wannan hanya, wanda yace sakamakon gudunmawar da suka bayar yakamata a rama alkhairi da alkhairi, musamman duba da yadda zabe yake karatowa.
Daga karshe Shugaban yayi kira ga al’ummar yankunan da su kara kwantar da hankulansu domin kungiyar matasan ba za ta gajiya ba wajen kiran Gwamnatin a halin da al’ummar suka samu kansu a ciki.