Daga: Zakariyya Adam Jigirya

A ranar Asabar, 18 ga Oktoba, 2025, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, Ph.D, ya kaddamar da sababbin gine-gine guda biyar (5) da suka ƙunshi azuzuwa goma (10), ofishin malamai da kujerun zama, domin inganta yanayin koyarwa a Makarantar GISS K/Maiyaki, da ke cikin karamar hukumar Kiru, Jihar Kano.

Wannan aiki, wanda ya kasance wani ɓangare na shirin dan majalisar na ci gaban ilimi a mazabarsa, ya sami halartar manyan baki daga hukumomi daban-daban. Cikin wadanda suka halarci bikin akwai Babban Darakta daga Ma’aikatar Upper Niger Development Authority, Mista Joshua Hassan, da kuma dan kwangilar da ya aiwatar da aikin, Alhaji Sani ’Yar Adua, tare da wakilan P.T.A/SBMC, shugaban makarantar da mai taimaka wa dan majalisar (SA), Ashiru Pilot.

A yayin taron, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana cewa ginin zai taimaka wajen rage cunkoson dalibai a ajujuwa da inganta yanayin karatu da koyarwa. Ya kara da cewa, “babu ci gaban al’umma face idan aka inganta ilimi, saboda haka zamu ci gaba da zuba jari a fannin ilimi domin gina kyakkyawar makoma ga ‘ya’yanmu.”

Masu halarta sun yaba da wannan kokari na dan majalisar, suna bayyana shi a matsayin abin koyi ga sauran wakilai, musamman wajen mayar da hankali kan ci gaban ilimi a yankunansu.

A karshe, an gudanar da addu’o’i na godiya da fatan alheri ga dan majalisar, tare da fatan Allah Ya saka masa da alheri ya kuma ba shi ikon ci gaba da irin wannan kokari mai albarka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano Dr. Gawuna Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Madakin Gini da Likita

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu  Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Kuma Shugaban hukumomin gudanar…

Remi Tinubu Ta Shawarci Matasa Su Rungumi Hakuri, Su Guji Dabi’ar Roƙo

Daga:  Abdullahi Bashir  Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta shawarci matasan…

Siyasar Ubangida Ita Ce Babbar Matsalar Da Ke Hana Najeriya Cigaba – Inji Comrade Nasiru Sulaiman Chamber

Daga: Kabir Getso Shugaban Hadakar Kungiyar Matasan Najeriya (United Nigeria Youth Congress), Comrade…

Majalisar Dokokin Kano Tayi Kira Kan Gaggauta Hukunta Wadanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Jihar Edo

Daga: Muhammad Adamu Abubakar Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kiran da a…