Daga: Shehu Suleiman Sharfadi

Gwamnatin Tarayya ta magantu a yayin da ta buƙaci kafafen yaɗa labarai da su riƙa yaɗa labaran da ke nuni da nasarorin da Najeriya ta samu a tsarin mulkin dimokiraɗiyya.

Alhaji Mohammed Idris Wanda ya kasance Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ne ya bayyana hakan a yayin bikin cikar Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) shekaru 70 da kafuwa, wanda aka gudanar a cibiyar Shehu Musa Yar’Adua da ke birnin Tarayya Abuja.

An ƙaddamar da wani littafi na tarihin ƙungiyar tare da kuma haɗawa da karramawa.

 

Ministan da yake jawabi a matsayin Babban Baƙon a wannan taron, Bisa wakilcin Shugaban Ƙasa Tinubu, kuma a matsayin Jagoran Biki, ya jaddada kusanci da goyon bayan da Shugaba Tinubu yake da shi ga kafafen yaɗa labarai a ƙasar nan.

Inda ya ce: “tun daga lokacin da ya kasance cikin masu gwagwarmayar tabbatar da zaɓen watan Yuni 12 tare da jarumai daga cikin ‘yan jaridu, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya kafa dangantaka mai ƙarfi da kafafen yaɗa labarai wanda ba a taɓa ganin makamancin sa a tarihin shugabannin Ƙasarnan ba.”

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Tarayya Ta Dauki Matakin Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Daga: Sani Ibrahim Gama Gwamnatin tarayya ta shiga tsakani don warware rikicin…

Dakarun Sojoji Sun Tarwatsa ‘Ƴan Ta’adda 600 a Cikin Mako Uku

Daga: Ibrahim Sani Gama Sojojin Nijeriya sun ci gaba da samun nasarori…

‘Yar Kasuwa Ta Samu Kyautar N500,000 Bayan Mayar Da N1m Da Ta Tsinta A Jos

Daga: Abdullahi Bashir Wani fitaccen ɗan kasuwa kuma ɗan siyasa, Ambasada Abubakar…

Dalilan Da Yasa Gwamnatin Jihar Kano Ta Jaddada Aniyarta Na Ganin An Biya Diyyar Wadanda Aka Hallaka A Jihar Edo

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi  Wani babban kwamiti wanda gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba…