Daga: Ibrahim Sani Gama
Sojojin Nijeriya sun ci gaba da samun nasarori a yaƙin da suke da ‘yan ta’adda a Arewa maso Gabas.
A cikin makonni uku da suka gabata, dakarun rundunar “Operation Hadin Kai” sun hallaka sama da ‘yan ta’adda 600, ciki har da shugabannin Boko Haram da ISWAP.
Wannan nasarar ta samo asali ne daga ci gaba da kokarin kawar da ta’addanci tun farkon watan Yuni, bayan da ‘yan ta’adda suka kai hare-hare 12 a Jihar Borno, inda lamarin ya yi sanadiyyar rasa rayukan sojoji da fararen hula da dama.
A makon farko na watan, sojojin sun kashe ‘yan ta’adda 94.
Sai dai, an rasa jami’an tsaro 20, ciki har da sojoji da ‘yan sa-kai, yayin da wasu fiye da 20 suka jikkata.
Duk da wadannan nasarorin, har yanzu al’ummar yankin na ci gaba da rayuwa cikin fargaba saboda rashin tabbas da halin da ake ciki.