Kano – Al’ummar Kano Ta Arewa sun bayyana farin cikinsu da godiyarsu ga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), CFR, bisa ƙoƙarinsa na ganin an gabatar da ƙudirin kafa Federal Medical Centre (FMC) Gwarzo a Jihar Kano.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun bayyana cewa idan aka samu wannan cibiyar lafiya, za ta taimaka wajen sauƙaƙa wahalhalun da marasa lafiya ke fuskanta wajen neman ingantaccen magani a manyan asibitoci da ke nesa. Sun ce cibiyar za ta kuma samar da guraben aikin yi, ƙarfafa horar da ma’aikatan lafiya tare da bunƙasa bincike da ci gaban fannin kiwon lafiya.
Al’ummar sun ce wannan yunƙuri ya ƙara nuna irin jajircewar Sanata Barau wajen kawo ayyukan ci gaba da suka shafi rayuwar jama’a kai tsaye, musamman a Kano Ta Arewa.

A ƙarshe, sun yi addu’ar Allah Ya ba shi lafiya, hikima da ƙarfin guiwar ci gaba da wakiltar al’umma tare da ganin an kai ƙudirin zuwa matakin aiwatarwa domin al’ummar yankin su amfana da wannan muhimmin aiki.