Daga: Ibrahim Sani Gama

Jam’iyyar APC ta sanar da sake tsara ranar gudanar da zabukan fidda gwani na gwamna a jihohin Bauchi da Kwara zuwa ranar Juma’a, 22 ga Mayu, 2026.

Haka kuma jam’iyyar ta mayar da zabukan fidda gwani na ‘yan takarar Majalisar Dokokin Jihar Zamfara na mazabun Maradun I da Maradun II zuwa ranar Lahadi, 24 ga Mayu, 2026.

A cikin wata sanarwa da APC ta fitar a yammacin ranar Alhamis, jam’iyyar ta ce Kwamitin Gudanarwa na Kasa (NWC) ne ya amince da sauyin bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki.

Sanarwar ta ce an dauki matakin ne domin tabbatar da gudanar da zabukan fidda gwani cikin gaskiya, tsari, lumana da sahihanci.

Jam’iyyar ta bayyana cewa sauyin ya shafi zabukan fidda gwani na gwamna a Bauchi da Kwara ne kawai, da kuma na ‘yan majalisar jiha a mazabun Maradun I da Maradun II a Zamfara, yayin da sauran zabukan fidda gwani ba su samu wani sauyi ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gawuna Ya Yi Murabus Daga Shugabancin Bankin Lamuni Na Gidaje Na Tarayya

Daga: Mukhtar Yahaya Shehu  Shugaban Hukumar Gudanarwa ta Bankin Lamuni na Gidaje na…

Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda Ya Tantance Gwamnan Imo, Uzodinma, Domin Takarar Sanatan Imo ta Yamma a 2027

Daga: Abdullahi Bashir Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya tantance…

Jagororin jam’iyyar NNPP a ƙaramar hukumar Tudun wada bisa jagorancin Hon. Salisu Yusha’u Soja Sun jaddada mubaya’a ga sabon Shugaban Jam’iyyar na jiha Hon. Abdullahi Zubairu Abiya.

  Jagororin jam’iyyar NNPP a ƙaramar hukumar Tudun wada bisa jagorancin Hon.…

Cikin watanni 6 Karamar Hukumar Sule-Tankarkar Ta Bunkasa Da Manyan Ayyuka – Hon Tasi’u

Daga: Kabir Getso Shugaban Karamar Hukumar Sule Tankarkar Hon Tasi’u Adamu ya bayyana…