Daga: Abdullahi Bashir 

Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Barrista Mohammed Abdullahi Abubakar, SAN, ya fito a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na kujerar gwamna na jam’iyyar APC a jihar domin tunkarar babban zaben shekarar 2027.

Shugaban Kwamitin Gudanar da Zaben Fidda Gwanin Gwamna da na ‘Yan Majalisar Dokokin Jiha na APC a Bauchi, tsohon Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (AIG mai ritaya), John Bassey Abang, ne ya sanar da sakamakon da safiyar Asabar, inda ya bayyana cewa an gudanar da zaben ne a ranar Juma’a, 22 ga Mayu, 2026.

A cewarsa, Mohammed Abdullahi Abubakar ya samu kuri’u 57,517, lamarin da ya ba shi nasara a kan sauran ‘yan takara shida da suka fafata a zaben.

Ya ce tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya samu kuri’u 26,001, yayin da Nura Manu Soro ya samu kuri’u 13,638.

Sauran wadanda suka shiga takarar sun hada da Bala Maijama’a A. Wunti wanda ya samu kuri’u 13,648 da kuma Kabir Baba Ma’aji da ya samu kuri’u 8,157.

Sakamakon zaben ya tabbatar da Mohammed Abdullahi Abubakar a matsayin dan takarar APC na gwamna a Bauchi domin babban zaben shekarar 2027.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Jihar Kano Ta Gargadi Maniyyata Kan Bin Ka’idojin Saudiyya Domin Gudanar da Aikin Hajji Cikin Nasara

Daga: Shehu Suleiman Sharfadi  Gwamnatin jihar Kano ta ja hankalin maniyyatan jihar…

Da Dumi-Dumi: Ƙaramin Ministan Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Rage Talauci Ya Yi Murabus

Ƙaramin Ministan Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Dr. Yusuf Tanko…

Sallah: Hukumar Tace Fina-Finai ta Kano Ta Sanya Sabbin Ka’idoji Kan Adaidaita Sahu, DJ Da Gidajen Wasanni

Daga: Muhammad Adamu Abubakar  Hukumar Tace Fina-Finai da Dabi’u ta Jihar Kano ta…

Rashin Guraben Tsayawa: Jama’a Na Kuka Da Gwamnatin Jihar Kano

Daga: Ibrahim Sani Gama Shugabancin Kungiyar matuka manyan motocin Tifa na jihar Kano…