
Daga: Shehu Suleiman Sharfadi
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya bi sahun manyan baki da sarakunan gargajiya domin murnar zagayowar ranar cika shekaru 25 da kafuwar mai martaba sarkin fune Dakta Saleh Idris ibn usman a kan karagar mulki.
Taron mai cike da tarihi wanda ya gudana a garin Fune dake Damagum a jihar Yobe, ya samu halartar manyan shugabanni, masu rike da sarautar gargajiya, da masu hannu da shuni don karrama wannan gagarumin hidima na sarki.
A yayin bikin, Mai Girma Mataimakin Gwamnan ya kuma halarci daurin auren Fatiha na ‘ya’yan Wazirin Fune, Mai Girma Mataimakin Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Idi Barde.
A wajen nuna zumunci da hadin kai, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo ya kasance Waliyyi (Mai kula) ga angon Kabir Idi Barde, inda ya gabatar da addu’o’i da fatan alheri da kwanciyar hankali.
Da yake jawabi bayan taron, mataimakin gwamnan ya taya mai martaba sarkin Fune murnar cika shekaru 25 a kan karagar mulki, inda ya yaba da jajircewarsa na samar da hadin kai, kiyaye kayayyakin tarihi, da inganta al’adu.
Ya kuma mika sakon taya murna ga sabbin ma’auratan, inda ya yi addu’ar Allah ya sa zaman nasu ya kasance cikin soyayya, fahimta, da wadata.
Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo ya jaddada kudirin gwamnatin jihar Kano na karfafa alaka da cibiyoyin gargajiya da hada kai a fadin jihohin kasar domin samun zaman lafiya, kwanciyar hankali a fadin kasarnan.