Daga: Shehu Suleiman sharfadi
Jim kadan bayan rantsar da Sabon Mataimakin Gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo ya kai ziyara karamar hukumar Gwarzo domin shaida karbar katin jam’iyyar APC na Sanata Bello Hayatu Gwarzo.
Mataimakin Gwamnan wanda ke tare da manyan ‘yan siyasa, ya samu kyakkyawar tarba daga dandazon al’umma da suka fito kan Titi domin taya shi murna tare da yi masa fatan alkhairi a sabon mukamin nasa

Akan hanyar sa daga kano zuwa gwarzo ya kwashi saoi da dama kafin ya karasa garin gwarzo sakamakon daruruwan mutane da suka fito kan hanya domin tarbarsa.
Wakilinmu na Ofishin Mataimakin Gwamna ya rawaito cewa, akwai fitattun yan siyasa a garin Gwarzo ciki har da tsohon mataimakin gwamnan jihar kano injiniya Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo da sanata Bello Hayatu da tsohon kwamishina Alhaji Ibrahim Dan Azumi da sauran wasu da dama.