Daga: Shehu Suleiman Sharfadi
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo, ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi Sayyadi Barhama Dan Almajiri, Mataimakin Babban Limamin Masallacin Juma’a na Taibah da ke Rijiyar Lemo, wanda ya rasu a ranar Talata bayan gajeriyar rashin lafiya yana da shekaru 70 a duniya.

Marigayin malamin addinin ya kasance babban yayan Barrista Bashir Dan Almajiri. Ya rasu ya bar mata guda daya, ’ya’ya takwas da jikoki.
Yayin ziyarar, Garo ya bayyana rasuwar fitaccen malamin addinin da cewa, “hakika wannan babban rashi ne ba ga iyalansa kadai ba, har ma da al’ummar Musulmi da daukacin Jihar Kano baki daya.”

Mataimakin Gwamnan ya kuma baiwa iyalansa da yan uwa hakurin jure rashin tare kuma da yi masa adduar fatan samun rahamar subhanahu wa ta’ala.