Daga: Adamu Dabo
A yau laraba dubban al’ummar jihar Kano daga sassa daban-daban tareda jerin gwannon kusoshin jam’iyar NNPP suka tarbi Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf a yayin dawowarsa daga aikin Hajjin shekarar 2025
Jirgin da ya zo da gwamnan da ayarinsa daga kasar Saudiyya ya fara sauka a jihar ikko da misalin karfe 2:50 na rana.
Daga nan sai jirgin ya baro jihar ikko zuwa jihar Kano,inda ya sauka da misalin karfe 3:04 na rana
Jim kadan bayan saukar jingin dimbin jama’a da suka tarbeshi suka Kuma raka gwamnan daga filin jirgin sauka da tashi na Malam Aminu Kano zuwa gidan gwamnatin jihar kano a tafiyar kasa da mintuna ashirin zuwa gidan gwamnati ta hanyar titin Murtala Mohammed sai da aka kwashe sama da awa biyar.
A yayin tafiyar mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ya dagawa mutane hannu a Wani yanayi na nuni da jin dadi da godiya ga alummar jihar Kano
Wakilinmu dake fadar gwamnatin jihar Kano Adamu Dabo ya rawaito cewar Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsaya a shateletalan gidan gwamnatin jihar Kano inda yayi jawabin godiya ga alummar jihar Kano dama magoya bayan jam’iyar NNPP