Daga: Shehu Suleiman Sharfadi 

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo, ya jagoranci zaman sulhu tsakanin masu neman takarar kujerar Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Rogo da Karaye, domin tabbatar da hadin kai da fahimtar juna a tsakanin ’yan jam’iyyar APC.

Wata sanarwa da daya daga cikin masu taimakawa Mataimakin Gwamnan kan harkokin yada labarai, Salmanu Rabi’u Gwarzo, ya fitar ta bayyana cewa zaman sulhun ya kai ga cimma matsaya tsakanin ’yan takarar, inda Alhaji Ibrahim Ahmad Karaye ya amince da janyewa Alhaji Abdullahi Sani Rogo takara cikin mutuntawa da fahimtar juna.

Taron ya gudana ne a gaban Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa, tare da wasu jiga-jigan jam’iyyar daga kananan hukumomin Karaye da Rogo.

Daga cikin wadanda suka halarci zaman sulhun akwai Alhaji Balarabe Isyaku Karaye, tsohon Shugaban Karamar Hukumar Karaye, Alhaji Naseer Abdullahi Dutsen Amare, tsohon Dan Majalisar Jiha mai wakiltar Karaye, da kuma Alhaji Idi Zare Rogo.

An gudanar da zaman sulhun ne a yammacin ranar Alhamis a ofishin Mataimakin Gwamna da ke gidan gwamnati.

Mahalarta taron sun jaddada bukatar ci gaba da zaman lafiya, hadin kai da kuma karfafa dankon zumunci a tsakanin ’ya’yan jam’iyyar APC.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Abincin Da Ake Bai Wa Alhazan Najeriya A Hajji

Daga: Abdullahi Bashir Hukumar Alhazai ta Kasa, National Hajj Commission of Nigeria…

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Dakile Satar Fasaha a Fannin Buga Littattafai

Daga: Ibrahim Sani Gama Gwamnatin Tarayya ta jaddada kudirinta na kawo karshen satar…

Mawuyacin Halin Da Makarantun Firamare Da Sakandire Na Langel A Ƙaramar Hukumar Tofa Ke Ciki

Daga:  Aliyu Ahmad Makarantun firamare da sakandire da ke ƙauyen Langel a…

Hukumar Kula Da Kayayyakin Amfanin Gona Ta Shawarci Al’umma Su Tabbatar Da Ingancin Kaya

Daga: Muhammad Adamu Abubakar  Hukumar kula da kayayyakin amfanin gona da ake shigowa…