Daga: Mas’ud Mato Garo
Shugaban Karamar Hukumar Kabo, Comr. Lawan Najume Kabo, ya jagoranci raba takardun daukar aikin koyarwa ga malamai 120 da Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta baiwa ‘yan karamar hukumar Kabo a yau Litinin, inda aka baiwa kowanne malami tallafin Naira Dubu Ashirin domin kudin mota.

A taron rabon takardun da aka gudanar a sakatariyar karamar hukumar, Shugaban ya bayyana cewa wannan mataki na gwamnati na da nufin inganta fannin ilimi da rage rashin aikin yi a yankin. Ya ce an zabi malaman ne daga cikin ‘yan asalin karamar hukumar bisa cancanta, kuma za su fara aiki nan take a makarantun firamare da sakandare dake fadin karamar hukumar.
Comr. Najume ya kara da cewa kudi N20,000 da aka baiwa kowane malami tallafi ne domin sauwaka musu halin tafiya zuwa makarantun da aka tura su. Haka zalika, ya bukaci sabbin malaman da su yi aiki tukuru, cikin gaskiya da amana domin ganin sun sauke amanar da gwamnati ta dora musu.