Daga: Sani Idris Maiwaya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira ga fitattun mawakan Najeriya da suka haɗa da Burna Boy da Davido da Asake da sauran attajiran masana’antar nishaɗi da su kafa gidauniyoyi domin tallafa wa marasa galihu.

Ta ce duk da cewa mallakar motocin alfarma irin su Maybach da Rolls-Royce abu ne mai kyau, hakan bai kamata ya hana su ware wani ɓangare na arzikinsu don taimaka wa masu sana’o’in dogaro da kai ba.

“Ya kamata mu ga Burna Boy da Asake da Davido da sauran fitattun mawaka suna da gidauniyoyi da ke taimaka wa talakawa. Akwai masu sayar da barkono da kayan lambu da kubewa da gyada da kuma masu soyar da ƙosai da ke buƙatar tallafi,” in ji ta.

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta kuma ba da labarin wata matashiya ‘yar jami’a daga Abuja wadda ta fara sana’ar soyar da ƙosai bayan ta rasa aikin yi.

A yayin taron, Sanata Remi Tinubu ta kuma rabawa ƙananan ‘yan kasuwa 2,000 a Jihar Kogi tallafin kuɗi na Naira 50,000 ga kowane mutum domin ƙarfafa sana’o’insu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Example Post for WordPress

This is a sample post created to test the basic formatting features…

Matsalar Tsaro Na Barazanar Dakile Noman Ridi a Arewacin Najeriya — Danliti Y.Y. Dawanau

Daga: Nura Garba Jibrin Kungiyar ’Yan Kasuwa da Masu Safarar Ridi ta Ƙasa,…

Gwamnatin Tarayya Ta Daga Kudin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000 Daga 2027

Daga: Abdullahi Muhammad Abuja — Gwamnatin Tarayya ta amince da karin kudin jarabawar…

An bayyana shugabar hukumar taimakekeniyar lafiya ta jihar Kano kachima Dr. Rahila Aliyu Mukhtar amatsyin Mace wadda baza amance da ita ba a harkokin lafiya a jihar Kano.

An bayyana shugabar hukumar taimakekeniyar lafiya ta jihar Kano kachima Dr. Rahila…