Daga: Abdullahi Bashir
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ware Naira biliyan 46 domin sake gina titin sauka da tashin jiragen sama na Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.
Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama da Raya Sararin Samaniya ya bayyana cewa, aikin na daga cikin shirye-shiryen gwamnatin tarayya na inganta tsaro da samar da ingantattun kayayyakin more rayuwa a manyan filayen jiragen saman ƙasar.

A cewarsa, titin jiragen saman na Kano ya dade yana buƙatar cikakken gyara saboda yawan amfani da shi da kuma muhimmancin filin jirgin saman ga zirga-zirgar fasinjoji da harkokin kasuwanci a Arewacin Najeriya.
Ana sa ran fara aikin nan ba da jimawa ba, yayin da gwamnati ta ce zai taimaka wajen inganta harkokin sufurin jiragen sama da bunƙasa tattalin arzikin jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.