Daga: Zakariyya Adam Jigirya
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya mahukunta da kafatanin ma’aikatan Rediyon Tarayya (Federal Radio Corporation of Nigeria) murnar cika shekaru 75 da kafuwa, yayin da kafar ta cimma wannan gagarumin mataki a ranar 1 ga Afrilu, 2026.

Shugaban ƙasar ya kuma miƙa jinjina ga Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta Ƙasa, tare da daukacin hukumomin da ke aiki kafada da kafada da FRCN, bisa wannan muhimmin biki.
Tinubu ya bayyana FRCN a matsayin wata kafa ko cibiyar watsa labarai mai tasiri, wacce ke taka rawar gani a Najeriya da ma nahiyar Afirka baki ɗaya, inda ya jaddada cewa ita ce mafi girman cibiyar rediyo a Afirka, mai tashoshin FM guda 47 da kuma tashoshi shida na shiyyoyi.
Ya kuma lura da yadda FRCN ta taka muhimmiyar rawa wajen inganta sadarwar ci gaba tsakanin shugabanni da al’umma sama da shekaru saba’in, takan zama gada mai ƙarfi ta musayar bayanai, ilimi da nishaɗi.
A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar, ya bayyana cewa Shugaba Tinubu na ganin FRCN ta adana tarihin Najeriya ta hanyoyi masu armashi tun daga zamanin mulkin mallaka zuwa bayan samun ‘yanci, inda take zama tushen bincike ga shugabanni, ɗalibai da masana.

Shugaban ƙasar ya kuma yaba da yadda tashar ke zama makaranta ga ƙwararrun masu watsa labarai, furodusoshi da injiniyoyin sauti a nahiyar Afirka.
Yayin da FRCN ke cika shekaru 75, Shugaba Tinubu ya buƙaci cibiyar da ta ci gaba da sauke nauyin da aka ɗora mata, bisa taken ta na, “Uplifting the People and Uniting the Nation.”