Kimanin Matasa ’yan Gwagwarmaya su goma sha biyar (15) ne Suka rabauta da samun tallafin babura daga Shugaban Karamar Hukumar Dala, Alhaji Suraj Ibrahim Imam, domin ƙarfafa ayyukansu da inganta rayuwarsu.

Da yake jawabi yayin ƙaddamar da rabon tallafin baburan, Alhaji Suraj Ibrahim Imam ya bayyana cewa tallafin da aka bai wa matasan ’yan gwagwarmaya ba alfarma ba ce, illa cancanta , duba da irin gudummawar da suke bayarwa.

Yana Mai Cewar nan gaba kaɗan, za a ƙaddamar da wani tallafi na musamman ga mata 200 Dake Karamar Hukumar Dala.

A nata jawabin, Shugabar Shugabannin Kananan Hukumomi ta Jihar Kano
Hajiya Sa’adatu Yusha’u Soja, ta yaba da wannan kyakkyawan shiri, tare da taya matasan da suka amfana murna. Ta jinjinawa Gwamnan Jihar Kano bisa yadda yake bai wa shugabannin kananan hukumomi cikakken goyon baya domin aiwatar da ayyukan da za su amfani al’ummar Kano.

Taron ya samu halartar Shugaban Karamar Hukumar Dawakin topa, Alhaji Anas Dan Maliki, da Mataimakin Shugaban karamar hukumar Dala alhaji Abdul’aziz Dayyabu Ahmad mai turare, kansuloli nadaddu da zababbu taron ya Gudana a Sakatariyar Karamar Hukumar ta Dala

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Mataimakin Gwamnan Kano Ya Kai Ziyarar Farko K/H Gwarzo Bayan Rantsar Da Shi

Daga: Shehu Suleiman sharfadi  Jim kadan bayan rantsar da Sabon Mataimakin Gwamnan…

Gidauniyoyi Sun Ceto Wasu Yara Dake Tituna a Kano, Sun Saka Su Cikin Farin Ciki

Daga: Saminu Ibrahim Magashi A wani mataki na nuna jinkai da kula da…

Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Wasan Sada Zumunta Na Shiyyar Arewa Maso Yamma

Daga: Shehu Suleiman sharfadi Hukumar kula da wasanni ta kasa ta shirya…

EFCC Ta Dakatar Da Asusun Gwamnatin Jihar Osun Kwanaki 10 Kafin Zabe

Daga: Abdullahi Bashir Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa…